< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
Out of the depths I have cried to thee, O Jehovah.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Lord, hear my voice. Let thine ears be attentive to the voice of my supplications.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
If thou, Jehovah, should note iniquities, O Lord, who could stand?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
But there is forgiveness with thee, that thou may be feared.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
I wait for Jehovah. My soul waits, and in his word do I hope,
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
my soul for the Lord more than watchmen for the morning, watchmen for the morning.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
O Israel, hope in Jehovah, for with Jehovah there is loving kindness, and with him is plentiful redemption.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
And he will redeem Israel from all his iniquities.

< Zabura 130 >