< Zabura 130 >
1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
(Sang til Festrejserne.) Fra det dybe råber jeg til
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
o Herre hør min Røst! Lad dine Ører lytte til min tryglende Røst!
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Tog du Vare, HERRE, på Misgerninger, Herre, hvo kunde da bestå?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
Men hos dig er der Syndsforladelse, at du må frygtes.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
Jeg håber. på HERREN, min Sjæl håber på hans Ord,
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
på Herren bier min Sjæl mer end Vægter på Morgen, Vægter på Morgen.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Israel, bi på HERREN! Thi hos HERREN er Miskundhed, hos ham er Forløsning i Overflod.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
Og han vil forløse Israel fra alle dets Misgerninger,