< Zabura 13 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Har yaushe, ya Ubangiji? Za ka manta da ni har abada ne? Har yaushe za ka ɓoye fuskarka daga gare ni?
Müzik şefi için - Davut'un mezmuru Ne zamana dek, ya RAB, Sonsuza dek mi beni unutacaksın? Ne zamana dek yüzünü benden gizleyeceksin?
2 Har yaushe zan yi kokawa da tunanina kuma kowace rana in kasance da damuwa a zuciyata? Har yaushe abokin gābana zai yi nasara a kaina?
Ne zamana dek içimde tasa, Yüreğimde hep keder olacak? Ne zamana dek düşmanım bana üstün çıkacak?
3 Ka dube ni ka amsa mini, ya Ubangiji Allahna. Ka ba da haske ga fuskata, ko in yi barci cikin mutuwa;
Gör halimi, ya RAB, yanıtla Tanrım, Gözlerimi aç, ölüm uykusuna dalmayayım.
4 abokin gābana zai ce, “Na sha ƙarfinsa,” kuma abokan gābana za su yi murna sa’ad da na fāɗi.
Düşmanlarım, “Onu yendik!” demesin, Sarsıldığımda hasımlarım sevinmesin.
5 Amma na dogara a kan ƙaunarka marar ƙarewa; zuciyata tana farin ciki a cikin cetonka.
Ben senin sevgine güveniyorum, Yüreğim kurtarışınla coşsun.
6 Zan rera ga Ubangiji gama ya yi mini alheri.
Ezgiler söyleyeceğim sana, ya RAB, Çünkü iyilik ettin bana.

< Zabura 13 >