< Zabura 13 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Har yaushe, ya Ubangiji? Za ka manta da ni har abada ne? Har yaushe za ka ɓoye fuskarka daga gare ni?
Salmo de Davi, para o regente: Até quando, SENHOR, te esquecerás de mim? Para sempre? Até quando tu esconderás de mim o teu rosto?
2 Har yaushe zan yi kokawa da tunanina kuma kowace rana in kasance da damuwa a zuciyata? Har yaushe abokin gābana zai yi nasara a kaina?
Até quando refletirei em minha alma, [tendo] tristeza em meu coração o dia todo? Até quando o meu inimigo se levantará contra mim?
3 Ka dube ni ka amsa mini, ya Ubangiji Allahna. Ka ba da haske ga fuskata, ko in yi barci cikin mutuwa;
Olha [para mim, e] ouve-me, SENHOR meu Deus; ilumina os meus olhos, para que eu não adormeça [na] morte.
4 abokin gābana zai ce, “Na sha ƙarfinsa,” kuma abokan gābana za su yi murna sa’ad da na fāɗi.
Para que meu inimigo não diga: Eu o venci; e meus inimigos se alegrem, se eu vier a cair.
5 Amma na dogara a kan ƙaunarka marar ƙarewa; zuciyata tana farin ciki a cikin cetonka.
Mas eu confio em tua bondade; em tua salvação meu coração se alegrará;
6 Zan rera ga Ubangiji gama ya yi mini alheri.
Cantarei ao SENHOR, porque ele tem me feito muito bem.