< Zabura 13 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Har yaushe, ya Ubangiji? Za ka manta da ni har abada ne? Har yaushe za ka ɓoye fuskarka daga gare ni?
Pak’ ombia, ry Iehovà? Ho haliño’o nainai’e hao iraho? Pak’ombia ty hañetaha’o laharañe amako?
2 Har yaushe zan yi kokawa da tunanina kuma kowace rana in kasance da damuwa a zuciyata? Har yaushe abokin gābana zai yi nasara a kaina?
Sikal’ombia ty hitsakoreako an-troko ao ty haoreako, ie añ’ovako ao lomoñandro? Ampara’ te ombia ty hañonjonañe ty rafelahikoo ambone ahy?
3 Ka dube ni ka amsa mini, ya Ubangiji Allahna. Ka ba da haske ga fuskata, ko in yi barci cikin mutuwa;
Vazohò, naho toiño iraho, ry Iehovà Andrianañahareko; hazavao o masokoo; tsy mone hiroroako ty firoron-kavilasy;
4 abokin gābana zai ce, “Na sha ƙarfinsa,” kuma abokan gābana za su yi murna sa’ad da na fāɗi.
Vaho hanao ty hoe i rafelahikoy: rinebako re; ke hirebeha’ o malaiñ’ ahikoo t’ie mibolatitse.
5 Amma na dogara a kan ƙaunarka marar ƙarewa; zuciyata tana farin ciki a cikin cetonka.
Fe fiatoako ty figahiñan’ arofo’o; hirebeha’ ty troko i fandrombaha’oy.
6 Zan rera ga Ubangiji gama ya yi mini alheri.
Ho saboeko t’Iehovà, amy te nampibodobodoe’e.

< Zabura 13 >