< Zabura 13 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Har yaushe, ya Ubangiji? Za ka manta da ni har abada ne? Har yaushe za ka ɓoye fuskarka daga gare ni?
For the Chief Musician. A Psalm of David. How long, O LORD, wilt thou forget me for ever? how long wilt thou hide thy face from me?
2 Har yaushe zan yi kokawa da tunanina kuma kowace rana in kasance da damuwa a zuciyata? Har yaushe abokin gābana zai yi nasara a kaina?
How long shall I take counsel in my soul, having sorrow in my heart all the day? how long shall mine enemy be exalted over me?
3 Ka dube ni ka amsa mini, ya Ubangiji Allahna. Ka ba da haske ga fuskata, ko in yi barci cikin mutuwa;
Consider [and] answer me, O LORD my God: lighten mine eyes, lest I sleep the [sleep of] death;
4 abokin gābana zai ce, “Na sha ƙarfinsa,” kuma abokan gābana za su yi murna sa’ad da na fāɗi.
Lest mine enemy say, I have prevailed against him; [lest] mine adversaries rejoice when I am moved.
5 Amma na dogara a kan ƙaunarka marar ƙarewa; zuciyata tana farin ciki a cikin cetonka.
But I have trusted in thy mercy; my heart shall rejoice in thy salvation:
6 Zan rera ga Ubangiji gama ya yi mini alheri.
I will sing unto the LORD, because he hath dealt bountifully with me.

< Zabura 13 >