< Zabura 13 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Har yaushe, ya Ubangiji? Za ka manta da ni har abada ne? Har yaushe za ka ɓoye fuskarka daga gare ni?
“For the leader of the music. A psalm of David.” How long, O LORD! wilt thou forget me for ever? How long wilt thou hide thy face from me?
2 Har yaushe zan yi kokawa da tunanina kuma kowace rana in kasance da damuwa a zuciyata? Har yaushe abokin gābana zai yi nasara a kaina?
How long shall I have anxiety in my soul for ever, And sorrow in my heart all the day? How long shall my enemy be exalted over me?
3 Ka dube ni ka amsa mini, ya Ubangiji Allahna. Ka ba da haske ga fuskata, ko in yi barci cikin mutuwa;
Look down and hear me, O LORD, my God! Enlighten my eyes, lest I sleep the sleep of death;
4 abokin gābana zai ce, “Na sha ƙarfinsa,” kuma abokan gābana za su yi murna sa’ad da na fāɗi.
Lest my enemy say, “I have prevailed against him!” Lest my adversaries rejoice, when I am fallen.
5 Amma na dogara a kan ƙaunarka marar ƙarewa; zuciyata tana farin ciki a cikin cetonka.
Yet will I trust in thy goodness; My heart shall rejoice in thy salvation;
6 Zan rera ga Ubangiji gama ya yi mini alheri.
I will sing to the LORD, that he hath dealt kindly with me.

< Zabura 13 >