< Zabura 13 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Har yaushe, ya Ubangiji? Za ka manta da ni har abada ne? Har yaushe za ka ɓoye fuskarka daga gare ni?
For the Leader. A Psalm of David. How long, O LORD, wilt Thou forget me for ever? How long wilt Thou hide Thy face from me?
2 Har yaushe zan yi kokawa da tunanina kuma kowace rana in kasance da damuwa a zuciyata? Har yaushe abokin gābana zai yi nasara a kaina?
How long shall I take counsel in my soul, having sorrow in my heart by day? How long shall mine enemy be exalted over me?
3 Ka dube ni ka amsa mini, ya Ubangiji Allahna. Ka ba da haske ga fuskata, ko in yi barci cikin mutuwa;
Behold Thou, and answer me, O LORD my God; lighten mine eyes, lest I sleep the sleep of death;
4 abokin gābana zai ce, “Na sha ƙarfinsa,” kuma abokan gābana za su yi murna sa’ad da na fāɗi.
Lest mine enemy say: 'I have prevailed against him'; lest mine adversaries rejoice when I am moved.
5 Amma na dogara a kan ƙaunarka marar ƙarewa; zuciyata tana farin ciki a cikin cetonka.
But as for me, in Thy mercy do I trust; my heart shall rejoice in Thy salvation.
6 Zan rera ga Ubangiji gama ya yi mini alheri.
I will sing unto the LORD, because He hath dealt bountifully with me.

< Zabura 13 >