< Zabura 13 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Har yaushe, ya Ubangiji? Za ka manta da ni har abada ne? Har yaushe za ka ɓoye fuskarka daga gare ni?
How long, O Jehovah? Will thou forget me forever? How long will thou hide thy face from me?
2 Har yaushe zan yi kokawa da tunanina kuma kowace rana in kasance da damuwa a zuciyata? Har yaushe abokin gābana zai yi nasara a kaina?
How long shall I take counsel in my soul, having sorrow in my heart all the day? How long shall my enemy be exalted over me?
3 Ka dube ni ka amsa mini, ya Ubangiji Allahna. Ka ba da haske ga fuskata, ko in yi barci cikin mutuwa;
Consider and answer me, O Jehovah my God. Lighten my eyes, lest I sleep the death,
4 abokin gābana zai ce, “Na sha ƙarfinsa,” kuma abokan gābana za su yi murna sa’ad da na fāɗi.
lest my enemy say, I have prevailed against him, lest my adversaries rejoice when I am moved.
5 Amma na dogara a kan ƙaunarka marar ƙarewa; zuciyata tana farin ciki a cikin cetonka.
But I have trusted in thy loving kindness. My heart shall rejoice in thy salvation.
6 Zan rera ga Ubangiji gama ya yi mini alheri.
I will sing to Jehovah because he has dealt bountifully with me.