< Zabura 129 >

1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
Hac ilahisi Gençliğimden beri bana sık sık saldırdılar; Şimdi söylesin İsrail:
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
“Gençliğimden beri bana sık sık saldırdılar, Ama yenemediler beni.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
Çiftçiler saban sürdüler sırtımda, Upuzun iz bıraktılar.”
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
Ama RAB adildir, Kesti kötülerin bağlarını.
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
Siyon'dan nefret eden herkes Utanç içinde geri çekilsin.
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
Damlardaki ota, Büyümeden kuruyan ota dönsünler.
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
Orakçı avucunu, Demetçi kucağını dolduramaz onunla.
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
Yoldan geçenler de, “RAB sizi kutsasın, RAB'bin adıyla sizi kutsarız” demezler.

< Zabura 129 >