< Zabura 129 >

1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
Muchas veces me persiguieron desde mi juventud. Que [lo] diga ahora Israel:
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
Muchas veces me persiguieron desde mi juventud, Pero no prevalecieron contra mí.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
Los aradores araron sobre mi espalda. Hicieron largos surcos.
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
Yavé es justo, Cortó las cuerdas de los perversos.
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
Sean avergonzados y vueltos atrás Todos los que aborrecen a Sion.
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
Sean como [la] hierba de las azoteas Que se marchita antes de crecer,
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
Con la cual el cosechero no llena su mano, Ni el regazo el que ata manojos.
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
Ni le dicen los que pasan: La bendición de Yavé sea sobre ustedes, Los bendecimos en el Nombre de Yavé.

< Zabura 129 >