< Zabura 129 >
1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
Pogosto so me prizadeli od moje mladosti, naj sedaj reče Izrael,
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
pogosto so me prizadeli od moje mladosti, vendar niso prevladali zoper mene.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
Orači so orali na mojem hrbtu; svoje brazde so naredili dolge.
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
Gospod je pravičen; razsekal je vrvi zlobnih.
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
Naj bodo zbegani in obrnjeni nazaj vsi, ki sovražijo Sion.
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
Naj bodo kakor trava na hišnih strehah, ki ovene preden zraste,
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
s čimer kosec ne napolni svoje roke niti kdor veže snope svojega naročja.
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
[Naj] niti tisti, ki gredo mimo, ne rečejo: »Nad vami naj bo Gospodov blagoslov. Blagoslavljamo vas v Gospodovem imenu.«