< Zabura 129 >

1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
Cântico dos degraus: Diga Israel: Desde minha juventude muitas vezes me afligiram.
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
Desde minha juventude, muitas vezes me afligiram, porém não prevaleceram contra mim.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
Lavradores lavraram sobre minhas costas, fizeram compridos os seus sulcos.
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
O SENHOR é justo; ele cortou as cordas dos perversos.
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
Sejam envergonhados, e voltem para trás todos os que odeiam a Sião.
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
Sejam como a erva dos telhados, que se seca antes que cresça.
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
Com que o ceifeiro não enche sua mão, nem o braço daquele que amarra os molhos.
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
Nem também os que passam, dizem: A bênção do SENHOR seja sobre vós; nós vos bendizemos no nome do SENHOR.

< Zabura 129 >