< Zabura 129 >

1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
Muitas vezes me angustiaram desde a minha mocidade, diga agora Israel:
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
Muitas vezes me angustiaram desde a minha mocidade, todavia não prevaleceram contra mim.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
Os lavradores araram sobre as minhas costas: compridos fizeram os seus sulcos.
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
O Senhor é justo: cortou as cordas dos impios.
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
Sejam confundidos, e voltem para traz, todos os que aborrecem a Sião.
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
Sejam como a herva dos telhados, que se secca antes que a arranquem.
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
Com a qual o segador não enche a sua mão, nem o que ata os feixes enche o seu braço.
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
Nem tão pouco os que passam digam: A benção do Senhor seja sobre vós: nós vos abençoamos em nome do Senhor.

< Zabura 129 >