< Zabura 129 >
1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
Ein Lied im höhern Chor. Sie haben mich oft gedrängt von meiner Jugend auf, so sage Israel,
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
sie haben mich oft gedrängt von meiner Jugend auf; aber sie haben mich nicht übermocht.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
Die Pflüger haben auf meinen Rücken geackert und ihre Furchen lang gezogen.
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
Der HERR, der gerecht ist, hat der Gottlosen Seile abgehauen.
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
Ach daß müßten zu Schanden werden und zurückkehren alle, die Zion gram sind!
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
Ach daß sie müßten sein wie das Gras auf den Dächern, welches verdorrt, ehe man es ausrauft,
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
von welchem der Schnitter seine Hand nicht füllt noch der Garbenbinder seinen Arm
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
und die vorübergehen nicht sprechen: “Der Segen des HERRN sei über euch! wir segnen euch im Namen des HERRN”!