< Zabura 129 >
1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
Cantique graduel. Dès mon jeune âge ils m'ont beaucoup opprimé, (qu'ainsi parle Israël!)
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
dès mon jeune âge ils m'ont beaucoup opprimé, mais ils n'ont pu l'emporter sur moi.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
Ils ont déchiré mon dos, comme ceux qui labourent, ils y ont tracé de longs sillons.
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
L'Éternel est juste, Il a rompu les fers où me retenaient des impies.
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
Qu'ils soient confondus, et fassent retraite tous ceux qui haïssent Sion!
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
Qu'ils soient comme l'herbe des toits, qui sèche, avant d'être arrachée,
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
dont le moissonneur ne remplit point sa main, dont le lieur ne charge point son bras;
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
et les passants ne disent pas: « Que l'Éternel vous bénisse! Nous vous bénissons au nom de l'Éternel! »