< Zabura 129 >
1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
Cantique des degrés. Ils m’ont assez opprimé dès ma jeunesse, Qu’Israël le dise!
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
Ils m’ont assez opprimé dès ma jeunesse, Mais ils ne m’ont pas vaincu.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
Des laboureurs ont labouré mon dos, Ils y ont tracé de longs sillons.
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
L’Éternel est juste: Il a coupé les cordes des méchants.
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
Qu’ils soient confondus et qu’ils reculent, Tous ceux qui haïssent Sion!
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
Qu’ils soient comme l’herbe des toits, Qui sèche avant qu’on l’arrache!
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
Le moissonneur n’en remplit point sa main, Celui qui lie les gerbes n’en charge point son bras,
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
Et les passants ne disent point: Que la bénédiction de l’Éternel soit sur vous! Nous vous bénissons au nom de l’Éternel!