< Zabura 129 >

1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
En Jérusalem. Souvent ils m'ont attaqué dès ma jeunesse; que maintenant Israël dise:
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
Souvent ils m'ont attaqué dès ma jeunesse, et ils n'ont rien pu sur moi.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
Les pécheurs ont frappé sur mon dos; ils ont prolongé leur iniquité.
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
Le Seigneur en sa justice a brisé le cou des pécheurs.
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
Qu'ils soient confondus et mis en fuite, tous ceux qui haïssent Sion.
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
Qu'ils deviennent comme l'herbe des toits, qui sèche avant d'être arrachée,
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
Et qui ne remplit ni la main du faucheur ni le sein du botteleur.
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
Sur eux les passants n'ont point dit: Que la bénédiction du Seigneur soit avec tous; nous vous bénissons au nom du Seigneur.

< Zabura 129 >