< Zabura 129 >
1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
A Song of the Ascents. Often they distressed me from my youth, Pray, let Israel say:
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
Often they distressed me from my youth, Yet they have not prevailed over me.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
Over my back have ploughers ploughed, They have made long their furrows.
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
Jehovah [is] righteous, He hath cut asunder cords of the wicked.
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
Confounded and turn backward do all hating Zion.
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
They are as grass of the roofs, That before it was drawn out withereth,
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
That hath not filled the hand of a reaper, And the bosom of a binder of sheaves.
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
And the passers by have not said, 'The blessing of Jehovah [is] on you, We blessed you in the Name of Jehovah!'