< Zabura 129 >
1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
A song of ascents. “Often since my youth they have attacked me,” let Israel say.
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
“Often since my youth they have attacked me, yet they have not defeated me.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
The plowers plowed on my back; they made their furrows long.
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
Yahweh is righteous; he has cut the ropes of the wicked.”
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
May they all be put to shame and turned back, those who hate Zion.
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
May they be like the grass on the housetops that withers before it grows up,
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
that cannot fill the reaper's hand or the chest of the one who binds bundles of grain together.
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
May those who pass by not say, “May the blessing of Yahweh be on you; we bless you in the name of Yahweh.”