< Zabura 129 >
1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
A Song of Ascents. Many a time, have they harassed me from my youth, well may Israel say:
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
Many a time, have they harassed me from youth, yet have they not prevailed against me.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
Upon my back, have ploughmen ploughed, They have lengthened their furrow!
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
Yahweh, is righteous, He hath cut asunder the cords of the lawless.
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
Let all who hate Zion, be ashamed and shrink back:
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
Let them become like the grass of housetops, which, before it is pulled up, hath withered;
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
Wherewith no reaper, hath filled his hand, nor binder, his bosom:
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
Neither have the passers-by ever said, The blessing of Yahweh, be unto you, —We have blessed you in the Name of Yahweh.