< Zabura 129 >

1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
A Song of Ascents. 'Much have they afflicted me from my youth up', let Israel now say;
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
'Much have they afflicted me from my youth up; but they have not prevailed against me.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
The plowers plowed upon my back; they made long their furrows.
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
The LORD is righteous; He hath cut asunder the cords of the wicked.'
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
Let them be ashamed and turned backward, all they that hate Zion.
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
Let them be as the grass upon the housetops, which withereth afore it springeth up;
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
Wherewith the reaper filleth not his hand, nor he that bindeth sheaves his bosom.
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
Neither do they that go by say: 'The blessing of the LORD be upon you; we bless you in the name of the LORD.'

< Zabura 129 >