< Zabura 129 >

1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
Often have they fought against me from my youth, let Israel now say.
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
Often have they fought against me from my youth: but they could not prevail over me.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
The wicked have wrought upon my back: they have lengthened their iniquity.
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
The Lord who is just will cut the necks of sinners:
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
Let them all be confounded and turned back that hate Sion.
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
Let them be as grass on the tops of houses: which withered before it be plucked up:
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
Wherewith the mower filleth not his hand: nor he that gathereth sheaves his bosom.
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
And they that have passed by have not said: The blessing of the Lord be upon you: we have blessed you in the name of the Lord.

< Zabura 129 >