< Zabura 128 >
1 Waƙar haurawa. Masu albarka ne dukan masu tsoron Ubangiji, waɗanda suke tafiya a hanyoyinsa.
Canticum graduum. [Beati omnes qui timent Dominum, qui ambulant in viis ejus.
2 Za ka ci amfanin aikinka; albarku da wadata za su zama naka.
Labores manuum tuarum quia manducabis: beatus es, et bene tibi erit.
3 Matarka za tă zama kamar kuringar inabi mai’ya’ya a cikin gidanka;’ya’yanka maza za su zama kamar tohon zaitun kewaye da teburinka.
Uxor tua sicut vitis abundans in lateribus domus tuæ; filii tui sicut novellæ olivarum in circuitu mensæ tuæ.
4 Ta haka mai albarka yake wanda yake tsoron Ubangiji.
Ecce sic benedicetur homo qui timet Dominum.
5 Bari Ubangiji ya albarkace ka daga Sihiyona dukan kwanakin ranka; bari ka ga wadatar Urushalima,
Benedicat tibi Dominus ex Sion, et videas bona Jerusalem omnibus diebus vitæ tuæ.
6 bari kuma ka rayu ka ga’ya’ya’ya’yanka. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
Et videas filios filiorum tuorum: pacem super Israël.]