< Zabura 128 >

1 Waƙar haurawa. Masu albarka ne dukan masu tsoron Ubangiji, waɗanda suke tafiya a hanyoyinsa.
Canto dei pellegrinaggi. Beato chiunque teme l’Eterno e cammina nelle sue vie!
2 Za ka ci amfanin aikinka; albarku da wadata za su zama naka.
Tu allora mangerai della fatica delle tue mani; sarai felice e prospererai.
3 Matarka za tă zama kamar kuringar inabi mai’ya’ya a cikin gidanka;’ya’yanka maza za su zama kamar tohon zaitun kewaye da teburinka.
La tua moglie sarà come una vigna fruttifera nell’interno della tua casa; i tuoi figliuoli, come piante d’ulivo intorno alla tua tavola.
4 Ta haka mai albarka yake wanda yake tsoron Ubangiji.
Ecco, così sarà benedetto l’uomo che teme l’Eterno.
5 Bari Ubangiji ya albarkace ka daga Sihiyona dukan kwanakin ranka; bari ka ga wadatar Urushalima,
L’Eterno ti benedica da Sion, e vedrai il bene di Gerusalemme tutti i giorni della tua vita,
6 bari kuma ka rayu ka ga’ya’ya’ya’yanka. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
e vedrai i figliuoli dei tuoi figliuoli. Pace sia sopra Israele.

< Zabura 128 >