< Zabura 128 >

1 Waƙar haurawa. Masu albarka ne dukan masu tsoron Ubangiji, waɗanda suke tafiya a hanyoyinsa.
A Song of the Ascents. O the happiness of every one fearing Jehovah, Who is walking in His ways.
2 Za ka ci amfanin aikinka; albarku da wadata za su zama naka.
The labour of thy hands thou surely eatest, Happy [art] thou, and good [is] to thee.
3 Matarka za tă zama kamar kuringar inabi mai’ya’ya a cikin gidanka;’ya’yanka maza za su zama kamar tohon zaitun kewaye da teburinka.
Thy wife [is] as a fruitful vine in the sides of thy house, Thy sons as olive plants around thy table.
4 Ta haka mai albarka yake wanda yake tsoron Ubangiji.
Lo, surely thus is the man blessed who is fearing Jehovah.
5 Bari Ubangiji ya albarkace ka daga Sihiyona dukan kwanakin ranka; bari ka ga wadatar Urushalima,
Jehovah doth bless thee out of Zion, Look, then, on the good of Jerusalem, All the days of thy life,
6 bari kuma ka rayu ka ga’ya’ya’ya’yanka. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
And see the sons of thy sons! Peace on Israel!

< Zabura 128 >