< Zabura 128 >
1 Waƙar haurawa. Masu albarka ne dukan masu tsoron Ubangiji, waɗanda suke tafiya a hanyoyinsa.
The song of greces. Blessid ben alle men, that dreden the Lord; that gon in hise weies.
2 Za ka ci amfanin aikinka; albarku da wadata za su zama naka.
For thou schalt ete the trauels of thin hondis; thou art blessid, and it schal be wel to thee.
3 Matarka za tă zama kamar kuringar inabi mai’ya’ya a cikin gidanka;’ya’yanka maza za su zama kamar tohon zaitun kewaye da teburinka.
Thi wijf as a plenteous vyne; in the sidis of thin hous. Thi sones as the newe sprenges of olyue trees; in the cumpas of thi bord.
4 Ta haka mai albarka yake wanda yake tsoron Ubangiji.
Lo! so a man schal be blessid; that dredith the Lord.
5 Bari Ubangiji ya albarkace ka daga Sihiyona dukan kwanakin ranka; bari ka ga wadatar Urushalima,
The Lord blesse thee fro Syon; and se thou the goodis of Jerusalem in alle the daies of thi lijf.
6 bari kuma ka rayu ka ga’ya’ya’ya’yanka. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
And se thou the sones of thi sones; se thou pees on Israel.