< Zabura 128 >
1 Waƙar haurawa. Masu albarka ne dukan masu tsoron Ubangiji, waɗanda suke tafiya a hanyoyinsa.
A song of ascents. Happy all who fear the Lord, who walk in his ways.
2 Za ka ci amfanin aikinka; albarku da wadata za su zama naka.
You will eat what your hands have toiled for, and be happy and prosperous!
3 Matarka za tă zama kamar kuringar inabi mai’ya’ya a cikin gidanka;’ya’yanka maza za su zama kamar tohon zaitun kewaye da teburinka.
Like a fruitful vine shall your wife be in the innermost room of your house: your children, like olive shoots, round about your table.
4 Ta haka mai albarka yake wanda yake tsoron Ubangiji.
See! This is the blessing of the man who fears the Lord.
5 Bari Ubangiji ya albarkace ka daga Sihiyona dukan kwanakin ranka; bari ka ga wadatar Urushalima,
The Lord shall bless you from Zion. You will see Jerusalem nourish all the days of your life.
6 bari kuma ka rayu ka ga’ya’ya’ya’yanka. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
You will see your children’s children. Peace upon Israel.