< Zabura 128 >
1 Waƙar haurawa. Masu albarka ne dukan masu tsoron Ubangiji, waɗanda suke tafiya a hanyoyinsa.
“A psalm of the steps, or the goings up.” Happy is he who feareth the LORD, Who walketh in his ways!
2 Za ka ci amfanin aikinka; albarku da wadata za su zama naka.
Thou shalt eat the labor of thy hands; Happy shalt thou be, and it shall be well with thee!
3 Matarka za tă zama kamar kuringar inabi mai’ya’ya a cikin gidanka;’ya’yanka maza za su zama kamar tohon zaitun kewaye da teburinka.
Thy wife shall be like a fruitful vine within thy house; Thy children like olive-branches round about thy table.
4 Ta haka mai albarka yake wanda yake tsoron Ubangiji.
Behold! thus happy is the man who feareth the LORD!
5 Bari Ubangiji ya albarkace ka daga Sihiyona dukan kwanakin ranka; bari ka ga wadatar Urushalima,
Jehovah shall bless thee out of Zion, And thou shalt see the prosperity of Jerusalem all the days of thy life;
6 bari kuma ka rayu ka ga’ya’ya’ya’yanka. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
Yea, thou shalt see thy children's children. Peace be to Israel!