< Zabura 128 >

1 Waƙar haurawa. Masu albarka ne dukan masu tsoron Ubangiji, waɗanda suke tafiya a hanyoyinsa.
Blessed are all who fear Jehovah, who walk in his ways.
2 Za ka ci amfanin aikinka; albarku da wadata za su zama naka.
For thou shall eat the labor of thy hands. Happy thou shall be, and it shall be well with thee.
3 Matarka za tă zama kamar kuringar inabi mai’ya’ya a cikin gidanka;’ya’yanka maza za su zama kamar tohon zaitun kewaye da teburinka.
Thy wife shall be as a fruitful vine in the innermost parts of thy house, thy sons like olive plants round about thy table.
4 Ta haka mai albarka yake wanda yake tsoron Ubangiji.
Behold, thus shall the man be blessed who fears Jehovah.
5 Bari Ubangiji ya albarkace ka daga Sihiyona dukan kwanakin ranka; bari ka ga wadatar Urushalima,
Jehovah bless thee out of Zion, and see thou the good of Jerusalem all the days of thy life.
6 bari kuma ka rayu ka ga’ya’ya’ya’yanka. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
Yea, see thou thy son's sons. Peace be upon Israel.

< Zabura 128 >