< Zabura 127 >

1 Waƙar haurawa. Ta Solomon. In ba Ubangiji ne ya gina gida ba, masu gininta suna wahala a banza ne. In ba Ubangiji ne yake tsaron birni ba, masu tsaro suna yin tsaro a banza.
Rwiyo rworwendo rwaSoromoni. Kana Jehovha asingavaki imba, vavaki vayo vanoshandira pasina. Kana Jehovha asingachengeti guta, varindi vanomira vakarinda pasina.
2 Banza ne ka farka da wuri ka koma da latti, kana fama don abincin da za ka ci, gama yakan ba da barci ga waɗanda yake ƙauna.
Hazvina maturo kumuka mangwanani nokunonoka kuvata, uchitambudzikira zvokudya, nokuti anopa hope kuna vaanoda.
3 ’Ya’ya maza gādo ne daga Ubangiji, yara lada ne daga gare shi.
Vanakomana inhaka inobva kuna Jehovha, vana mubayiro unobva kwaari.
4 Kamar kibiyoyi a hannun jarumi haka’ya’ya mazan da aka haifa wa mutum a ƙuruciya.
Semiseve mumaoko emhare ndizvo zvakaita vanakomana voujaya.
5 Mai albarka ne mutumin da korinsa sun cika da su. Ba za a kunyata su ba sa’ad da suke ƙarawa da abokan gābansu a ɗakin shari’a.
Akaropafadzwa murume ane goba rizere navo. Havanganyadziswi pavanokakavadzana navavengi vavo pasuo.

< Zabura 127 >