< Zabura 127 >
1 Waƙar haurawa. Ta Solomon. In ba Ubangiji ne ya gina gida ba, masu gininta suna wahala a banza ne. In ba Ubangiji ne yake tsaron birni ba, masu tsaro suna yin tsaro a banza.
A Song of Ascents. Solomon’s. If, Yahweh, build not the house, in vain, have the builders of it toiled thereon, If, Yahweh, watch not the city, in vain, hath the watchman kept awake:
2 Banza ne ka farka da wuri ka koma da latti, kana fama don abincin da za ka ci, gama yakan ba da barci ga waɗanda yake ƙauna.
Vain for you, —to be early in rising, to be late in lying down, to be eating the bread of wearisome toil, So, would he give his beloved one sleep.
3 ’Ya’ya maza gādo ne daga Ubangiji, yara lada ne daga gare shi.
Lo! an inheritance from Yahweh, are children, A reward, the fruit of the womb:
4 Kamar kibiyoyi a hannun jarumi haka’ya’ya mazan da aka haifa wa mutum a ƙuruciya.
As arrows in the hand of a warrior, so, are the children of young men.
5 Mai albarka ne mutumin da korinsa sun cika da su. Ba za a kunyata su ba sa’ad da suke ƙarawa da abokan gābansu a ɗakin shari’a.
How happy the man who hath filled his quiver with them! They will not be ashamed, but will speak with enemies in the gate.