< Zabura 127 >

1 Waƙar haurawa. Ta Solomon. In ba Ubangiji ne ya gina gida ba, masu gininta suna wahala a banza ne. In ba Ubangiji ne yake tsaron birni ba, masu tsaro suna yin tsaro a banza.
A song of ascents. Of Solomon. Unless the Lord builds the house, those who build it labor in vain. Unless the Lord guards the city, the watchman wakes in vain.
2 Banza ne ka farka da wuri ka koma da latti, kana fama don abincin da za ka ci, gama yakan ba da barci ga waɗanda yake ƙauna.
In vain you rise early, and finish so late, and so eat sorrow’s bread; for he cares for his loved ones in their sleep.
3 ’Ya’ya maza gādo ne daga Ubangiji, yara lada ne daga gare shi.
Children are a gift of the Lord, the fruit of the womb, a reward.
4 Kamar kibiyoyi a hannun jarumi haka’ya’ya mazan da aka haifa wa mutum a ƙuruciya.
Like arrows wielded by warriors, are the children of youth.
5 Mai albarka ne mutumin da korinsa sun cika da su. Ba za a kunyata su ba sa’ad da suke ƙarawa da abokan gābansu a ɗakin shari’a.
Happy the man who has filled his quiver full of them. He will not be ashamed when he speaks with enemies in the gate.

< Zabura 127 >