< Zabura 126 >

1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
Un cántico para los peregrinos que van a Jerusalén. ¡Cuando el Señor trajo a Israel de vuelta del cautiverio, fue como si estuviéramos soñando!
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Reímos mucho y cantamos de alegría. Las otras naciones dijeron, “El Señor ha hecho cosas maravillosas por su pueblo”.
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
Ciertamente el Señor ha hecho cosas maravillosas por nosotros. ¡Cuánto nos alegramos!
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Por favor, vuelve y ayúdanos otra vez, Señor. Renuévanos como los arroyos de agua que renuevan el desierto de Negev.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
Los que siembran en lágrimas cosecharán con gritos de alegría!
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Los que lloran cuando salen a sembrar su semilla cantarán de júbilo cuando lleven la cosecha a casa.

< Zabura 126 >