< Zabura 126 >

1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
En sang ved festreisene. Da Herren lot Sions fanger vende tilbake, var vi som drømmende;
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
da fyltes vår munn med latter, og vår tunge med jubel, da sa de iblandt hedningene: Store ting har Herren gjort imot disse.
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
Store ting har Herren gjort imot oss; vi blev glade.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Herre, la våre fanger vende tilbake likesom bekker i sydlandet!
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
De som sår med gråt, skal høste fryderop.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
De går gråtende og bærer den de strør ut; de kommer hjem fryderop og bærer sine kornbånd.

< Zabura 126 >