< Zabura 126 >
1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
Lapho iNkosi ibuyisa abathunjiweyo beZiyoni, saba njengabaphuphayo.
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Umlomo wethu wasugcwala uhleko, lolimi lwethu ukuhlabelela. Basebesithi phakathi kwezizwe: INkosi ibenzele izinto ezinkulu.
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
INkosi isenzele izinto ezinkulu; siyathokoza.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Buyisa, Nkosi, ukuthunjwa kwethu, njengezifula zeningizimu.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
Abahlanyela ngezinyembezi bazavuna ngentokozo.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Yena ohamba ahambe ekhala inyembezi, ephethe inhlanyelo yokuhlanyela, isibili uzabuya ethokoza, ethwele inyanda zakhe.