< Zabura 126 >

1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
«Ωιδή των Αναβαθμών.» Ότε ο Κύριος επανέφερε τους αιχμαλώτους της Σιών, ήμεθα ως οι ονειρευόμενοι.
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Τότε ενεπλήσθη το στόμα ημών από γέλωτος και η γλώσσα ημών από αγαλλιάσεως· τότε έλεγον μεταξύ των εθνών, Μεγαλεία έκαμε δι' αυτούς ο Κύριος.
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
Μεγαλεία έκαμεν ο Κύριος δι' ημάς· ενεπλήσθημεν χαράς.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Επίστρεψον, Κύριε, τους αιχμαλώτους ημών, ως τους χειμάρρους εν τω νότω.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
Οι σπείροντες μετά δακρύων εν αγαλλιάσει θέλουσι θερίσει.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Όστις εξέρχεται και κλαίει, βαστάζων σπόρον πολύτιμον, ούτος βεβαίως θέλει επιστρέψει εν αγαλλιάσει, βαστάζων τα χειρόβολα αυτού.

< Zabura 126 >