< Zabura 126 >

1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
Ein Wallfahrtslied. Als der HERR einst Zions Mißgeschick wandte,
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Damals war unser Mund voll Lachens und unsre Zunge voll Jubels; damals sagte man unter den Heiden: »Der HERR hat Großes an ihnen getan!«
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
Ja, Großes hatte der HERR an uns getan: wie waren wir fröhlich!
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Wende, o HERR, unser Mißgeschick gleich den Bächen im Mittagsland!
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
Die mit Tränen säen, werden mit Jubel ernten.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Wohl schreitet man weinend dahin, wenn man trägt den Samen zur Aussaat; doch jubelnd kehrt man heim, mit Garben beladen.

< Zabura 126 >