< Zabura 126 >
1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
Cantique de Maaloth. Quand l'Éternel ramena les captifs de Sion, nous étions comme ceux qui font un rêve.
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Alors notre bouche fut pleine de cris de joie, et notre langue de chants de triomphe. Alors on disait parmi les nations: L'Éternel a fait de grandes choses à ceux-ci.
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
L'Éternel nous a fait de grandes choses; nous en avons été joyeux.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Éternel, ramène nos captifs, comme les ruisseaux au pays du midi!
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
Ceux qui sèment avec larmes, moissonneront avec chants de triomphe.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Celui qui porte la semence pour la répandre, marche en pleurant; mais il reviendra en chantant de joie, quand il portera ses gerbes.