< Zabura 126 >

1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
The song of grecis. Whanne the Lord turnede the caitifte of Sion; we weren maad as coumfortid.
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Thanne oure mouth was fillid with ioye; and oure tunge with ful out ioiyng. Thanne thei schulen seie among hethene men; The Lord magnefiede to do with hem.
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
The Lord magnefiede to do with vs; we ben maad glad.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Lord, turne thou oure caitifte; as a stronde in the south.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
Thei that sowen in teeris; schulen repe in ful out ioiyng.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Thei goynge yeden, and wepten; sendynge her seedis. But thei comynge schulen come with ful out ioiyng; berynge her handfullis.

< Zabura 126 >