< Zabura 126 >

1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
When Yahweh brought [us Israeli people] back to Jerusalem (OR, enabled us Israelis to prosper again), [it was wonderful]; it seemed as though [SIM] we were dreaming.
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
We were extremely happy, and we [SYN] continued shouting joyfully. Then the [other] people-groups said about us, “Yahweh has done great things for them!”
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
[And we say, “Yes], Yahweh [truly] has done great things for us, and we are [very] happy.”
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Yahweh, when it rains, water flows in the streams again [after they were dry] [SIM]. Similarly, enable our nation to become great again like it was before.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
We cried when we planted [seeds because it was hard work preparing the soil that had not been plowed for many years]; [now we want to] shout joyfully because we are gathering a [big] harvest.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Those who cried as they carried the [bags of] seeds [to the fields] will shout joyfully when they bring the crops [to their houses at harvest time].

< Zabura 126 >