< Zabura 126 >
1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
“A song of the degrees.” When the Lord bringeth back again the captivity of Zion, then shall we be like dreamers.
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Then shall our mouth be filled with laughter, and our tongue with singing: then shall they say among the nations, Great things hath the Lord done for these.
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
Great things would the Lord have done for us, [whereat] we should be joyful.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Bring back again, O Lord, our captivity, like rivulets in arid land.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
Those that sow in tears shall reap with joyful song.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
He goeth forth indeed and weepeth, that beareth the seed for sowing; but he will surely come with joyful song when he beareth [home] his sheaves.