< Zabura 126 >
1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
A song for pilgrims going up to Jerusalem. When the Lord brought his people back from captivity to Zion, it was as if we were dreaming!
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
We laughed so much, we sang for joy. The other nations said, “The Lord has done wonderful things for these people.”
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
The Lord certainly has done wonderful things for us. How happy we were!
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Please return and help us again, Lord. Renew us like streams of water that renew the Negev desert.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
Those who sow in tears will reap with shouts of joy!
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Those who weep as they go out to sow their seed will be singing in celebration when they carry the harvest home.