< Zabura 126 >
1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
When the lord brought back the captivity of Sion, we became like men comforted.
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Then was our mouth filled with gladness; and our tongue with joy. Then shall they say among the Gentiles: The Lord hath done great things for them.
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
The Lord hath done great things for us: we are become joyful.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Turn again our captivity, O Lord, as a stream in the south.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
They that sow in tears shall reap in joy.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Going they went and wept, casting their seeds. But coming they shall come with joyfulness, carrying their sheaves.