< Zabura 126 >

1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
A Canticle in steps. When the Lord turned back the captivity of Zion, we became like those who are consoled.
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Then our mouth was filled with gladness and our tongue with exultation. Then they will say among the nations: “The Lord has done great things for them.”
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
The Lord has done great things for us. We have become joyful.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Convert our captivity, O Lord, like a torrent in the south.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
Those who sow in tears shall reap in exultation.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
When departing, they went forth and wept, sowing their seeds. But when returning, they will arrive with exultation, carrying their sheaves.

< Zabura 126 >