< Zabura 126 >
1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
A song of ascents. When the LORD restored the captives of Zion, we were like dreamers.
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Then our mouths were filled with laughter, our tongues with shouts of joy. Then it was said among the nations, “The LORD has done great things for them.”
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
The LORD has done great things for us; we are filled with joy.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Restore our captives, O LORD, like streams in the Negev.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
Those who sow in tears will reap with shouts of joy.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
He who goes out weeping, bearing a trail of seed, will surely return with shouts of joy, carrying sheaves of grain.