< Zabura 126 >

1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
Wer ma ji wero kadhi e hekalu. Kane Jehova Nyasaye odwogo joma otwe Sayun, to ne ochalonwa mana lek.
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Ne wathungʼ gi nyiero kendo dhowa nopongʼ gi wende mor. Eka nowachore e dier ogendini niya, “Jehova Nyasaye osetimonegi gik madongo.”
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
Adier, Jehova Nyasaye osetimonwa gik madongo, omiyo wamor mokalo.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Duognwa gigewa, yaye Jehova Nyasaye, mondo wachal gi aore man Negev.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
Joma komo kodhi kaywak biro keyo ka wero wende mor.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Ngʼat madhi oko kaywak, kotingʼo kodhi mikomo, biro duogo ka wero wende mor, kotingʼo cham mosechiek.

< Zabura 126 >