< Zabura 126 >
1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
Der Herren hjemførte Zions Folk, som vendte tilbage, da vare vi som drømmende,
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
da blev vor Mund fyldt med Latter og vor Tunge med Frydesang, da sagde man iblandt Hedningerne: Herren har gjort store Ting imod disse.
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
Herren har gjort store Ting imod os; vi bleve glade.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Hjemfør, Herre! vore fangne, lig Sydlandets Strømme.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
De, som saa med Graad, skulle høste med Frydesang.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Den, som bærer Sæden, der saas, gaar sin Gang med Graad; men han skal komme med Frydesang, naar han hjembærer sine Neg.