< Zabura 125 >
1 Waƙar haurawa. Waɗanda suke dogara ga Ubangiji suna kama da Dutsen Sihiyona, wanda ba ya jijjiguwa amma dawwammame ne har abada.
En vallfartssång. De som förtrösta på HERREN, de likna Sions berg, som icke vacklar, utan förbliver evinnerligen.
2 Kamar duwatsun da sun kewaye Urushalima, haka Ubangiji ya kewaye mutanensa yanzu da har abada kuma.
Jerusalem omhägnas av berg, och HERREN omhägnar sitt folk, ifrån nu och till evig tid.
3 Sandar mulkin mugaye ba zai ci gaba da kasance a kan ƙasar da take rabon adalai ba, domin kada masu adalci su yi amfani da hannuwansu su aikata mugunta.
Ty ogudaktighetens spira skall icke förbliva över de rättfärdigas arvslott, på det att de rättfärdiga ej må uträcka sina händer till orättfärdighet.
4 Ka yi alheri, ya Ubangiji, ga waɗanda suke nagartattu, ga waɗanda suke masu aikata gaskiya a zuciyarsu.
Gör gott, o HERRE, mot de goda och mot dem som hava redliga hjärtan.
5 Amma waɗanda suka juye ga karkatattun hanyoyi Ubangiji zai kore su tare da masu aikata mugunta. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
Men dem som vika av på vrånga vägar, dem rycke HERREN bort tillika med ogärningsmännen. Frid vare över Israel!