< Zabura 125 >
1 Waƙar haurawa. Waɗanda suke dogara ga Ubangiji suna kama da Dutsen Sihiyona, wanda ba ya jijjiguwa amma dawwammame ne har abada.
Ко се узда у Господа, он је као гора Сион, не помеша се, остаје довека.
2 Kamar duwatsun da sun kewaye Urushalima, haka Ubangiji ya kewaye mutanensa yanzu da har abada kuma.
Око Јерусалима су горе, и Господ је око народа свог одсад и довека.
3 Sandar mulkin mugaye ba zai ci gaba da kasance a kan ƙasar da take rabon adalai ba, domin kada masu adalci su yi amfani da hannuwansu su aikata mugunta.
Јер неће остати скиптар безбожнички над делом праведничким, да не би праведници пружили руке своје на безакоње.
4 Ka yi alheri, ya Ubangiji, ga waɗanda suke nagartattu, ga waɗanda suke masu aikata gaskiya a zuciyarsu.
Учини, Господе, добро добрима и онима који су права срца.
5 Amma waɗanda suka juye ga karkatattun hanyoyi Ubangiji zai kore su tare da masu aikata mugunta. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
А који сврћу на криве путе, отераће Господ с онима који чине безакоње. Мир Израиљу!